LAIFIN RAHAMA SADAU, AFAKALLAH AND KANNYWOOD

Asalin Rahama Sadau yar rawar gala ce kafin Ali Nuhu ya kyalla ido ya hango ta da fahimtar cewa wannan yarinya za ta iya zama wata gagarumar jaruma. Kasancewar Alin ne ya kawo ta masana’antar hadi da cewa ta iya acting, kafin ka ce me, ta fara samun shahara yadda ta dusashe sauran taurari mata. Cikin abubuwan da su ka daga likkafar wannan yarinya aka san ta sosai bai rasa nasaba da kutsa kanta cikin rigingimu iri-iri tun shigowarta wannan masana’anta, watakila ta na ganin cewa ta hanyar saka kanta cikin rikice-rikice su ne za su dawwamar da tauraronta a sama ba tare da la’akari da irin al’ummar da ta sami kanta a ciki ba.

Rikicin baya bayan nan ba shi ne na farko, ko na biyu ko na uku ko hudu ba, shine rikici na biyar da ta sami kanta idan zamu iya tunawa. A farkon shigowarta masana’antar Kannywood ta sami rikici da babban jarumi Adam Zango yayin da ta je wajen da ya ke daukar wani fim nasa kuma ta tashi aikin tare da yin fashe-fashe, abinda ya kai su gurfana gaban kwamitin ladabtarwa na MOPPAN inda a karshe ta bada hakuri da alkawarin ba za’a sake ba. Rahama ta sake samun kanta cikin wani rikicin inda wani mai shirya fina-finai a Maiduguri ya dauke ta a matsayin jaruma amma sakamakon sabani da su ka samu ta je ta dauko masa sojoji wadanda su ka zo wajen daukar fim din su ka hargitsa shi yadda aikin bai yiwu ba. Ance sakamakon bakin cikin wannan hasara da Rahama ta jaza masa ya sa yayi hadari a hanyarsa ta dawowa inda ya mutu.

Ana nan sai gashi ta sake jajubo wata babbar rigimar wadda ta dauki hankali mutane a fadin kasar inda ta yi wata waka da wani mawaki mai suna ClassiQ inda ta ke rungumarsa. Wannan hoton bidiyo ya harzuka wasu mutane da ke ganin cewa bai dace ba, yadda sakamakon korafe-korafe ya sa kungiyar MOPPAN ta bakin Salisu Officer a jaridar Guardian in day a sanar da cewa “An kori Rahama gaba daya daga masana’antar…sakamakon rashin da’ar da ta nuna a wata waka da ta ke rungumar wani”. Kafin cimma wannan matsaya shugabannin na MOPPAN sun kai ruwa rana tsakaninsu inda wasu ke ganin a dakatar da ita shekaru uku amma masu ra’ayin a kore ta ya yi rinjaye inda mutane shida cikin goma su ka amince da korarta, ganin cewa Rahama duk da alkawuran da ta sha dauka a baya bai hana ta kaucewa rikice-rikice ba.

Ba dadewa da korarta ba sai ta sami gayyatar shahararren mawakin Amurka, Akon, tare da hadin gwiwar mai shirya fim na Nollywood Jeta Amata, zuwa cibiyar fina-finai ta duniya wato Hollywood. Akon ya sanar a shafinsa na tiwita cewa “Ya kamata mu karfafa matan mu da azama su zuwa ci gaba, karbarsu ya fi korarsu” a matsayin wani shagube ga hukumar MOPPAN. Kungiyar MOPPAN ta mika wannan hukunci na korar Rahama ga babban daraktan hukumar tace fina-finai ta Kano wato Afakallah, wanda ya saka hannun amincewa. Bayan nan sai Rahama ta ci gaba da harkokinta a wajen Kano ganin yadda likkafarta ta daukaka kuma ta ci gaba da yin harkokin fim nata na kanta da kuma a masana’antar Nollywood. Bayan lokaci ya ja sai Rahama ta fara kokarin yadda za ta dawo Kannywood a yafe mata kamar yadda wani jami’in MOPPAN ya shaida min a Kano cewa ta yi kokarin baiwa wani jami’in MOPPAN cin hanci na Naira dubu hamsin domin ya hada ganawarta da masu ruwa da tsaki a MOPPAN ko Allah zai sa su yafe mata ta dawo cikin masana’antar, abinda ya ki yayi.

Katsam a makon da ya gabata sai ga shi ta sake jawo wata babbar rigimar wadda ba ta taba yin irinta ba sakamakon saka wasu hotuna na ta da ke nuna tsiraicin bayanta, abinda ya ja wani wanda ba musulmi ya yi kalaman batanci ga Annabi Muhammadu. An ce Rahama ba ta cire, ko maidawa mutumin martini ba har na tsawon sa’o’i sama da ashirin. Kuma wasu cikin kawayenta sun yi kokarin hana ta saka wannan hotuna tun asali sanin yadda za su iya kawo cece-kuce. Anan ya kamata mutane su sani cewa a duk duniya, hatta a Amurka da kasashen yamma, akwai abinda ake ganin bai kamata a yi shi a idon jama’a ba, wanda ya sa dokar kasashe ke da hukunci kan abubuwa na bai dace ba. Irin wannan doka na daukar “Duk wani abu da ya jibanci yada wani abu cikin jama’a da ya danganci batsa, zagi ko abu mara kyaun gani da zai iya tada hankalin jama’a”. Wannan ya sa Kotun Kolin Amurka (kotun da ma ta halatta auren jinsi) ta tabbatar da wannan doka wajen hana furta kalaman zagi/ashar a duk wani shirin talabijin, musamman domin a kare yara masu tasowa. A shekarar 1984 lokacin da Madonna ta saki bidiyon wakarta “Like A Virgin” ta fuskanci caccakar jama’a har daga fadar Fafaroma. Haka ma wakar Salt N Pepa a shekarar 1991 wadda ke maganar jima’i (Lets talk about sex) da kuma wakar TLC “Aint too proud to be” da ire-iren wadannan wakokin duk sun fuskanci suka. Laifin Rahama anan shine a matsayinta na musulma ta san cewa akwai ka’aidar shiga wadda addini ya tanada a Qur’ani cewa dole mata su rufe wuraren da za su iya jan hankalin maza musammam daga kafada zuwa kasan kwauri a duk sanda su ke a bainar jama’a. Hikimar Qurani shine rufe wadannan wurare zai rage abubuwa irinsu fyade da sauransu, kuma bude su na iya kawo hadurra da matsaloli, musamman idan muka yi la’akari da cewa ganin bayanta a bude ya sa wani wanda ba musulmi ba ya yi kalaman batanci ga Annabi Muhammadu. Da ba ta saka wannan hoto ba ka ga irin wannan batanci da bai faru ba. A matsayin halin da Najeriya ke ciki na matsi da fushin matasa, yadda kwanan nan mun ga yadda zanga-zangar Endsar ta haifar da mummunar tarzoma, wannan kalamai nabatanci na iya rura wutar rikicin addini wadda ba za ta haifarwa kowa da mai ido ba. Amma dai Babban Sufeton yan sanda ya yi wuf ya umarci kwamishinan yan sanda na Kaduna ya gaggauta bincike.

Shi kuma Babban Daraktan hukumar tace fina-finai, Afakallah, nasa laifin na da yawa, domin kasancewar wanda MOPPAN ta tuntuba kuma ya sahale da korar Rahama tun asali, bai kamata ya dawo shi kadai ba tare da tuntunbar MOPPAN din ba wajen yi mata afuwa yadda ya ce hukumarsa za ta ci gaba da tace fina-finanta. Yin hakan ya karfafa Rahama wajen ci gaba da yin abinda duk ta ga dama da kuma zaizaiye ikon wannan kungiya a kan yayanta. Lokacin da aka sanar da baiwa Afakallah wannan mukami nasa, na yi matukar farin ciki ganin cewa ya fito daga wannan masana’anta don haka na dauka cewa zai kawo canji da aka dade ana tsammani a wannan masana’anta, amma daga dukkan alamu ya kasa. Sanin kowa ne cewa gwamna Kwankwaso abokin masana’antar Kannywood ne kuma ya karfafa ta ta hanyoyi da dama domin hatta ita wannan hukuma da Afakallah ke jagoranta shi ya kafa ta. Amma a bayyane ya ke cewa ba wani gwamna da ya jawo yan masana’antar cikin gwamnati irin gwamna Ganduje (duk da cewa a daya hannun kuma ana yiwa gwamnatinsa kallon ta na yi wa wasu yan masana’antar bita da kulli, idan mu ka duba yadda aka kama Naziru Sarkin waka da Sunusi Oscar), domin akalla yan masana’antar da dama sun sami mukamai a cikin gwamnatin. Bayan Afakallah, akwai Al-Kinana, Yahanasu Sani, Rashida Adamu, Nura Hussein, Ado Baffa (Marigayi), Ali Lilo da Ibrahim Ibrahim.

Masana’antar Kannywood ba taba samun irin wannan tagomashi ba kuma ya ci a ce wadannan jami’ai sun kawo wani gagarumin canji ta hanyar samar da hadin kai da tallafi na gwamnati wajen ci gaban masana’antar. Amma abin takaici kusan duk wadannan jami’ai bukatar gabansu su ke yi domin ba wata hujja a kasa wadda ta nuna sun kawo wani gagarumin canji. Shi kansa Afakallah wanda ke da mafi girman mukami cikinsu, a bayyane ya ke ya gaza musamman idan aka yi la’akari da ikirarin da daya daga cikin jagororin masana’antar, Hamisu Iyantama ya shaida min, cewa ya kasance shugaban kwamitin farfado da kasuwanci a masana’antar wanda Afakalla ya kafa. Cikin hira ta da shi ya tabbatar da cewa wannan kwamiti na su ya lalubo hanyoyi ingantattu wajen farfado da kasuwancin masana’antar wanda ya durkushe, ta kokarin farfado da sinimomi musamman marhaba, wanda abin bai dore ba. Kuma sun jawo hankulan masu gidajen kallo wajen ganin sun saka nuna fina-finan hausa a cikin jadawalinsu. Sannan ya kara da cewa sun yi kokarin yakar satar fasaha ta hanyar zuwa jihohi da dama domin jawon hankulan masu rarraba fina-finai su daina karbar kowanne fim sai da takardar shaidar hukumar tace fina-finai. Har ila yau kwamitin ya hada taro da yan downloading a gaban jami’an tsaro domin nuna musu illar satar fasaha. Haka nan sun yi kokarin samar da dandalin yanar gizo domin tallata fina-finan masana’antar. Abin tambaya shine menene dalilin da wadannan kyawawan shirye shirye ba su kai gaci ba? Iyantama ya dora laifin ga Afakallah da cewa bai iya mu’amala da jama’a ba kuma tsawon watannin da su ka kwashe su na wannan aiki hatta dan alawus na zaman aiki ko na tafiye-tafiye hukumar ba ta iya samar musu ba, yadda da kudaden aljihunsu su ka rika wannan aiki baya ga ajiye harkokinsu domin samarwa masana’antar mafita. Taron da su ka yi da yan downloading da jami’an tsaro ne kadai hukumar ta dauki nauyi. A karshe ma dutse a hannun riga su ka rabu da Afakallah ba tare da nuna wata godiya ba ko tabbatar da abubuwan da su ka kawo domin ci gaban masana’antar. Ya kamata Afakallah ya farka daga barci ya san cewa sauran shekaru biyu su ka rage masa, kuma idan ya gama su, cikin masana’antar dai zai dawo, don haka ya rage nasa ya yi amfani da lokacin da ya rage masa domin tabbatar da cewa ya bar bayan da zai yi alfahari da ita.

Ita kuwa masana’antar Kannywood, kamar yadda duk sauran al’amuran hausawa su ke a yau, ta kasance ba wani abu da za’a hadu ayi aiki tare domin gudu a tsira tare, kowa biyan gajeruwar bukatar sa ita ce a gabansa. Idan mu na da hankali, a yau ba mu da wata masana’anta wadda za ta iya samarwa dimbin matasan mu aikin yi da kudaden shiga kamar Kannywood. Domin kamar yadda na taba fada a wani rubutu na a baya, a yayin da marubucin fim ya dora bironsa a kan takarda, daga nan ya fara samar da ayyukan yi da su ka hada da jarumai, masu shiryawa, bada umarni, daukan hoto, masu tacewa, tsara wajen aiki, masu buga takardu, masu ababen hawa na haya, masu otal-otal, madinka, yan talla, masu kasuwanci, masu rarraba fim da tallansa, gidajen rediyoyi da talabijin kai hatta matan aure a gidajensu wadanda ke dafa abinci akai wurin daukar fim ko bada hayar sutura. A kalla akwai kimanin sana’o’i 26 da ke da alaka da yin harkar fim. MOPPAN ta gaza wajen samar da ingantaccen shugabanci a kungiyoyin kwararru (guilds) da ke karkashinta wanda ta hanyarsu za’a iya samarwa da yan masana’antar tallafi a karfafa su kuma idan ta kama a ladabtar da su. Yawancin wadannan kungiyoyi karkashin MOPPAN za ka samu a rarrabe su ke yadda da yawa na da shugabanci guda biyu masu hamayya da juna. Ita kanta MOPPAN din mu na iya cewa ba tsaye ta ke dakafufuwanta ba domin ba ta da ingantattun hanyoyin samun kudin shiga yadda wasu lokatai ko kudin haya ba sa iya biya daga asusun su.

Ginshikin kowacce masana’antar fim a duniya bayan saka jari ita ce samun ingantacciyar hanyar kyautar karramawa (Awards) domin ita ke jawo hankalin masu saka jari, samar da ingantattun fina-finai da kuma tabbatar da gogayya da azama ga duk wanda ke cikin masana’antar wajen ganin ya inganta abinda ya ke yi. An wayi gari a Kannywood yau babu wata kyautar karramawa ta azo gani sakamakon guda dayar da ake zaton za ta kai gaci an barta ta mutu, wadda ke nan kuma a yanzu masu jagorantarta baki ne wadanda, ba abinda za su samarwa masana’antar ce a gabansu ba sai dai abinda za su samu daga masana’antar. Ita kanta gwamnati Kano da tana da masu bata shawara da ta ware a kallah miliyan hamsin duk shekara domin samar da irin wannan karramawa ta gwamnati, ba don komai ba sai don zai habaka harkar a masana’antar yadda za ta iya kawowa jihar masu saka jari sannan za ta iya samun kudaden shiga ninkin abinda su ka saka duk shekara idan abin ya karbu, abinda su Afakallah da yan uwansa na Kannywood da ke cikin gwamnatin ya kamata a ce tuni sun saidawa gwamnati.

Ya kamata masu sana’a a masana’antar da kungiyoyi har da ita gwamnati, gaba dayanmu mu farka mu gane cewa wannan masana’anta tamkar saniya ce mai jiran tatsa, idan muka tashi tsaye za mu ci moriyar ta, amma idan mun ci gaba da son kai ba tare da la’akari da gina masana’antar ba, hakika za mu wuce mu bar ta, domin ko ka ki ko ka so, masana’antar fim ba abinda zai kauda ta, sai dai watakila idan mun wuce wasu za su zo su tatseta. 

Comments

Popular posts from this blog

MALAMAI SUN TAIMAKA WAJEN RUSA AREWA

JINNS: SPIRITUAL FANTASY OR SCIENTIFIC POSSIBILITY?

THE NORTHERN WAHALA!